

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gabanin zaben fidda gwani na manyan jam’iyyun siyasa guda biyu wato APC da PDP, masu neman tsayawa takara suna sayen daloli a fadin kasar nan, lamarin da ke janyo faduwar darajar naira.
An bayyana cewa dala ta yi tashin gwauron zabi tsakanin naira 550 zuwa 570 a watanni biyun da suka gabata, inda ta tashi zuwa naira 595 a kasuwar bayan fage a jiya.
Bincike ya nuna cewa darajar Naira na ci gaba da faduwa akan dala a kasuwannin bayan fage yayin da jama’a da dama ke neman kudaden kasashen waje da suka fara karanci.
A wani labarin kuma, mataimakin kakakin majalisar dokokin jihar Kano, Zubairu Hamza Massu, ya sauya sheka daga jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyar NNPP.
Zubairu Massu ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a wata wasika da ya aikewa shugaban jam’iyyar na mazabar Massu.
Dan majalisar ya kafa hujja da rigingimun da ke faruwa a jam’iyyar da rashin adalci da rashin bin dimokradiyya a matsayin dalilan da suka sa ya fice daga jam’iyyar.