Gwamna Badaru Abubakar ya bukaci matasan Arewacin Najeriya su kwantar da hankulan su game da kisan Filato

0 129

Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na Jihar Jigawa ya bukaci matasan Arewacin Najeriya su kwantar da hankulan su domin Jami’an tsaro suyi aikin su wajen zakulo mutanen da sukayi kisa a jihar Plateau.

Wannan na kunshe cikin wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman ga Maigirma Gwamnan Jihar Jigawa a Sabbin Kafafen Sadarwa Auwal Danladi Sankara ya rabawa manema labarai a Dutse.

A cewarsa, gwamnan ya bayyana hakan ne a lokacin da ya ziyarci Gwamnan Jihar Plateau Simon Bako Lalong a birnin Jos domin jajanta masa.

An rawaito cewa kimanin Matafiya Musulmai 25 ne suka fito daga Jihar Bauchi zuwa jihar Ondo aka kashe su a jihar.

Kazalika, Gwamna Badaru Abubakar ya ce tuni Jami’an tsaro suka fara gudanar da bincike kan lamurin tare da kama wadanda ake zargin da kashe matafiyan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: