

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Gwamna Bala Muhammad na Jihar Bauchi ya bukaci tsohon mataimakin shugaban Kasa Atiku Abubakar ya ajiye kudurin sa na tsayawa takara, domin ya mara masa baya, biyo bayan gogewar da yake da ita wajen ciyar da kasa gaba idan aka zabe shi a 2023.
Gwamna Jihar ta Bauchi, ya bayyana hakan ne a lokacin da ya bayyana a gidan talabijin na Channels Tv ta cikin shirin ‘‘Politics Today’’ inda ya yi karin haske kan rikice-rikicen da jam’iyar PDP take ciki.
Tsohon Ministan na birnin tarayya ya bayyana cewa yana da gogewa ta fuskar ciyar da kasa gaba, sannan Matashi ne shi mai cike da koshin lafiya.
Haka kuma ya ce Abokan sa da kudancin kasar nan, sunyi alkawarin mara masa baya matukar ya samu tikitin tsayawa takarar.
Kazalika, ya ce goyan bayan da kungiyar Dattawan Arewa suka yiwa masa, baya nufin masu neman takara a Jam’iyar PDP a Arewa su tsaya.