Gwamnan Jihar Zamfara ya rufe dukkan Kasuwannin da suke ci mako-mako a fadin Jihar saboda tsaro

0 78

Gwamnan Jihar Zamfara Bello Matawallen Maradun, ya sanar da dokar rufe dukkan Kasuwannin da suke ci Mako-Mako a fadin Jihar a wani mataki na inganta lamuran tsaro da yake cigaba da tabarbarewa a jihar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa NAN, ya rawaito cewa Gwamna Bello Matawalle ya bayyana hakan ne a lokacin da yake karbar Daliban Kwalegin Aikin Gona da Bakura wanda yan bindiga suka sake su bayan shafe kwanaki 12 a hannun su.

Gwamnan ya kuma, ce gwamnatin Jihar ta haramta sayar da Man fetur a bakin tituna, a wani mataki na hana kaiwa yan bindigar Man fetur.

Haka kuma, gwamnan Jihar ya haramta safarar Shanu da Itace a sassan jihar, inda ya kara da cewa dole ne a binciki masu safarar Abinci, domin tabbatar da cewa ba’a kaiwa yan bindigar ba.

Kazalika, Gwamnan ya bukaci mutanen Jihar su kai rahoton masu karya dokar da gwamnati ta shimfida.

Leave a Reply

%d bloggers like this: