Gwamnatin Buhari ce ta kara kudin makaranta na kwalejojin hadaka (FGC)

0 212

Ma’aikatar ilimi ta tarayya ta ce gwamnatin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ce ta sake duba sabon tsarin biyan kudin makaranta na kwalejojin hadin kai.

Hakan na kunshe ne a wasu takardu da aka samu daga ma’aikatar ilimi ta tarayya jiya a Abuja.

Takardun sun bayyana cewa sabon tsarin biyan kudin makaranta ya samu amincewar tsohon ministan ilimi, Adamu Adamu a karkashin mulkin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Wata majiya daga ma’aikatar da ta so a sakaya sunanta ta shaida wa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN  jiya a Abuja cewa kudaden karatu a kwalejojin hadin kan gwamnati kyauta ne amma ana son dalibai su biya wasu abubuwa kamar kudin litattafai, Unifos da ciyarwa da kudin dakunan kwana.

Idan dai ba a manta ba a shekarar 2020 ne gwamnatin tarayya ta karbi Naira 15,000 a matsayin kudin kwana ga sabbin dalibai, wanda ya kawo adadin kudin zuwa N50,500.

Ta sake duba kudin zuwa N30,000 a watan Mayu, inda ta kawo jimlar kudin zuwa N100,000.

Sai dai kuma ga daliban da suka dawo, gwamnatin tarayya ta biya N48,500 a matsayin jimillar kudin a shekarar 2020 sabanin N47,000 a shekarar 2023 na daliban kwana. NAN

Leave a Reply

%d bloggers like this: