

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Gwamnatin jihar Jigawa ta dauki mutane fiye da dubu daya aiki domin cike guraben aikin gwamnati a shekarar data gabata.
Shugaban ma’aikata na jiha, Alhaji Hussaini Ali Kila ne ya bayyana haka lokacin da yake tilawar nasarorin da ofishin sa ya samu a shekarar ta 2021 ta cikin shirin Gidan Radion Jigawa na musamman.
Ya ce an dauki daliban da suka sami shedar digiri mafi daraja karkashin tsarin gwamnati na daukar aiki kai tsaye da kuma bangaren kiwon lafiya dana ilimi.
Alhaji Hussaini Ali Kila ya cigaba da cewa an yiwa ma’aikata da dama karin girma, kari akan basu horo da sake horas dasu domin samun kwarewa wajen gudanar da ayyukansu.
Shugaban ma’aikatan ya kuma yabawa kudirin gwamnatin jiha na biyan albashi da fansho da kuma hakkokin ma’aikatan da suka bar aiki akan lokaci.
Daga nan ya yi kira ga ma’aikata su kara kokari wajen gudanar da ayyukansu, tare da gargadin cewa gwamnati ba zata amince da kin zuwa wurin aiki ko fashi ba.