Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da shirin ciyarwa a watan Ramadana, a wani mataki na rage al’umma da masu karamin karfi radadin da suke ciki

0 76

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da shirin ciyarwa a watan Ramadana, a wani mataki na rage Al’umma da masu karamin karfi radadin da suke ciki.

Da yake jawabi a lokacin kaddamar da shirin a harabar kamfanin buga takardu mallakin Jihar Kano, Mukaddashin Gwamna Dr Nasiru Yusif Gawuna, ya bukaci mambobin kwamatin su kasance masu yin gaskiya da adalci a lokacin gudanar da ayyukan su.

Dr Gawuna, wanda ya yi jawabi kan muhimmancin ciyar da masu karamin karfi musamman a watan Ramadana, ya bukaci mutane suyi amfani da wannan dama.

Tun farko a jawabinsa, Kwamishinan Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Karkokin Masarautu Alhaji Murtala Sule Garo, ya bayyana cewa gwamnatin Jihar ta ware Naira Miliyan 550 domin gudanar da ciyarwar a cibiyoyi 140 wanda Jihar ta ware, kuma 8 a cikin birnin Kano suke.

Kwamishinan ya ce daga cikin kayayyakin da aka ware domin ciyarwar sun hada da Shinkafa, Wake, Fulawa, Gero, Man Girki da kuma Manja.

Leave a Reply

%d bloggers like this: