Gwamnatin tarayya tace an bullo da shirin inganta rayuwar alumma ne da nufin rage kaso 70 na talauci da yan Najeriya ke ciki

0 69

Gwamnatin tarayya tace an bullo da shirin inganta rayuwar alumma ne a 2016, da nufin rage kaso 70 na talauci da yan Nigeria ke ciki.

Ministar jinkai da kula da jindadin jama-a ta kasa Hajia Sadiya Umar Farouk, ta bayyana hakan a wajen bikin kaddamar da shirin bunkasa kananan sanaoi na gwamnatin tarayya a jihar Jigawa.

Ministar wadda ta samu wakilcin babban sakataren ma’aikatar, Dr Nasiru Sani Gwarzo tace an yiwa mutane dubu 48,000 rijistar shiga shirin a jihar nan daga 2017 zuwa yanzu.

Inda kowannensu ya samu rancen naira dubu hamsin marar kudin ruwa daga gwamnatin tarayya domin fara sana-a.

An raba shirin kaso uku da suka hadar da na Trader money da Market money da kuma farmers money.

A sakon daya aike dashi wajen bikin, gwamna Muhammad Badaru Abubakar ta hannun shugaban ma’aikata, Alhaji Hussain Ali Kila ya yabawa gwamnatin tarayya bisa tallafawa jihar Jigawa a tsare tsarenta na yaki da fatara da talauci.

Leave a Reply

%d bloggers like this: