Hankali ma ba zai dauka ba idan aka ba ‘yan kwana-kwana damar rike bindiga, a cewar Majalisa

0 101

Majalisar wakila ta Najeriya ta bukaci gwamnatin Najeriya data yi watsi da matakin bai wa jami’an kashe wuta bindiga (kwana-kwana).

A baya gwamnati ta sanar da shirinta na mika wa majalisar dokoki kudirin yi wa dokar ‘yan kwana-kwana garambawul ta hanyar bai wa jami’an damar rike makamai don kare kansu daga hare-haren da ake kai masu a yayin gudanar da ayyukansu.

Sai dai majalisar ta bukaci gwamnatin ta dakatar da matakin.

Kamar yadda BBCHausa ta ruwato a rahotan ta, Honarabul Thomas Ereyitomi wanda ya gabatar da bukatar a gaban majalisar ya bayyana cewa hukumar ‘yan kwana-kwana hukuma ce ta farar hula ba ta tsaro ba.

Sannan ya ce hankali ma ba zai dauka ba idan aka ba su damar rike bindiga saboda ba sa bukatarta.

Leave a Reply

%d bloggers like this: