Hukumar jin dadin Alhazai zata gudanar da bita ga sabbin jamianta na kananan hukumomi

0 138

Hukumar jin dadin Alhazai ta jihar Jigawa zata gudanar da taron bitar sanin makamar aiki ga sabbin jamianta na kananan hukumomi wato center officers. 

Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da kakakin hukumar Murtala Usman Madobi ya sanyawa hannu.

Yace za a gudanar da bitar ne a ranar Talata shida ga watan Fabrairu a dakin taro na kungiyar maaikatan lafiya ta jihar Jigawa dake Dutse. Sanarwar ta kara da cewar za a gudanar da taron bitar ne karkashin jagorancin Darakta Janar na Hukumar Alhaji Ahmad Umar Labbo.

Leave a Reply

%d bloggers like this: