Hukumar kashe gobara ta kasa tace gobarar da aka samu a ginin ma’aikatar kudi yau da safe karama ce wacce ta shafi batira kadai

0 65

Hukumar kashe gobara ta kasa tace gobarar da aka samu a ginin ma’aikatar kudi yau da safe karama ce wacce ta shafi batira kuma an gaggauta dakile ta.

Kakakin hukumar, Abraham Paul, ya gayawa manema labarai cewa lamarin ya faru ne a kasan ginin ma’aikatar inda aka ajiye batiran.

Yace babu wanda ya rasu kuma babu wanda ya samu wani baban rauni. Amma akalla manyan batira 20 sun lalace.

A nasa jawabin, kakakin ma’aikatar ta kudi, Olajide Osundun, yace wutar ta tashi da misalin karfe 6 da mintuna 50 na safe lokacin da wasu ma’aikatan ma’aikatar suka ga hayaki na fitowa daga wajen.

Kakakin yace an shawo kan wutar bayan mutane sun kawo dauki.

Gobarar a ma’aikatar na zuwa ne kimanin makonni 2 bayan an samu wata babbar gobara a wata hukumar ta gwamnati.

Leave a Reply

%d bloggers like this: