

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Hukumar kashe gobara ta kasa tace gobarar da aka samu a ginin ma’aikatar kudi yau da safe karama ce wacce ta shafi batira kuma an gaggauta dakile ta.
Kakakin hukumar, Abraham Paul, ya gayawa manema labarai cewa lamarin ya faru ne a kasan ginin ma’aikatar inda aka ajiye batiran.
Yace babu wanda ya rasu kuma babu wanda ya samu wani baban rauni. Amma akalla manyan batira 20 sun lalace.
A nasa jawabin, kakakin ma’aikatar ta kudi, Olajide Osundun, yace wutar ta tashi da misalin karfe 6 da mintuna 50 na safe lokacin da wasu ma’aikatan ma’aikatar suka ga hayaki na fitowa daga wajen.
Kakakin yace an shawo kan wutar bayan mutane sun kawo dauki.
Gobarar a ma’aikatar na zuwa ne kimanin makonni 2 bayan an samu wata babbar gobara a wata hukumar ta gwamnati.