Hukumar kula da tsaftar muhalli ta jiha (JISEPA) ta kaddamar da aiki tsaftar muhalli na kwanaki goma a kananan hukumomi hudu dake yankin masarautar Hadejia

0 75

Hukumar kula da tsaftar muhalli ta jiha (JISEPA) ta kaddamar da aiki tsaftar muhalli na kwanaki goma a kananan hukumomi hudu dake yankin masarautar Hadejia.

Manajan daraktan hukumar, Injiniya Lawal Ahmed Zauma, ya bayyana haka a yayin kaddamar da aikin a garin Guri.

Yace aikin ya ka su kashi biyu wanda ya hada da kwashe shara a unguwanni da kasuwanni da yin feshin maganin sauro a makarantun kwana da asibitoci da kuma sauran gine-ginen hukumomin gwamnati.

Lawal Ahmed Zauma, ya ce manufar aikin itace tsaftace garuruwa domin kare al’umma daga kamuwa daga cututtuka masu yaduwa a sanadiyyar rashin tsaftar muhalli.

Manajan daraktan ya bukaci al’umma, musamman shugabannin kananan hukumomin Guri da Malam-Madori da Auyo da Hadejia da kungiyoyin ‘yan kasuwa dana kyautatatuwar zaman jama’a da su mara baya ga ma’aikatan hukumar, domin cimma nasarar tsaftace yankunan kananan hukumomin su.

Leave a Reply

%d bloggers like this: