

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Rundunar yansanda jihar jigawa na sanar da alumar jihar jigawa, musamman wadanda suka nemi shiga aikin dan sandan a shekarar 2021 a matsayin kurata, wadanda ba’a tantance ba, dasu hallara tare da takardun su gobe juma’a 11 ga watan fabareru, a hedkwatar Hakumar yan sanda ta jihar Jigawa da ke dutse babban birnin jiha, da misalign karfe 8 na safe, Domin a tantance su.
Sanarwar hakan ta fito ne daga bakin kakakin rundunar yan sandan jihar ASP Lawan Shiisu Adam, ta cikin wani sakon murya da ya aikewa gidan radio sawaba, da safiyar yau.
A cikin Sanarwar ta dakiku 36, Kakakin yace bata shafi wadanda aka tantance tun da fari ba.