

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Darakta Janar na hukumar bunkasa fasahar sadarwa ta kasa (NITDA), Kashifu Inuwa, ya sanar da cewa manhajar biyan albashi ta UTAS da kungiyar malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) take so a amince da ita, bata da inganci.
Kashifu Inuwa ya sanar da haka a jiya yayin da yake amsa tambayoyi daga manema labaran fadar shugaban kasa a karshen zaman ganawar majalisar zartarwa ta tarayya, wanda mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta a zauren fadar shugaban kasa dake Abuja.
A cewarsa, manhajar UTAS ta kasa samun nasara a gwajin ingancin da zai tabbatar da cancantarta wajen biyan albashi.
Idan za a iya tunawa dai, kungiyar ASUU ta shiga yajin aikin gargadi a ranar 14 ga watan Fabrairu domin matsawa gwamnatin tarayya ta biya mata bukatunta da suka hada da kudi naira tiriliya 1 da miliyan dubu 3.
Kungiyar tana kuma bukatar gwamnatin tarayya ta amince da manhajar UTAS domin maye gurbin IPPIS wajen biyan albashi.