Yawan mutanen da annobar corona ta shafa a Najeriya ya kai dubu arba’in da tara da dari takwas da casa’in da biyar, bayan an sake gano mutane dari hudu da goma dauke da cutar a jiya.
Daga cikin adadin, sama da mutane dubu talatin da bakwai sun warke kuma an sallamesu a jihoshi talatin da shida na kasarnan, da babban birnin tarayya, Abuja.
- Tsananin zafi yasa an rufe daukacin makarantun dake kasar Sudan ta kudu
- An sake sassauta dokar hana zirga-zirgar babura masu kafa uku a wasu sassan jihar Adamawa
- Sanata Abdul’Aziz Yari ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa Shugaba Bola Tinubu addu’a
- Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 14 a kauyen Dogon Noma-Ungwan Gamo
- Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaga da Magumeri da Gubio a majalisar wakilai ya raba kayan abinci ga iyalai 5,000
Cutar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu cikin sa’o’i ashirin da hudu, kuma yawan wadanda annobar ta kashe kawo yanzu ya kai dari tara da tamanin da daya.
Hakan ya fito ne daga hukumar dakile yaduwar cututttuka ta kasa NCDC, wacce ke jagorantar kula da barkewar cutar corona, cuta mai kama da mura, wacce ta yadu zuwa kasashe sama da dari biyu kuma ta harbi sama da mutane miliyan biyu.