Yawan mutanen da annobar corona ta shafa a Najeriya ya kai dubu arba’in da tara da dari takwas da casa’in da biyar, bayan an sake gano mutane dari hudu da goma dauke da cutar a jiya.
Daga cikin adadin, sama da mutane dubu talatin da bakwai sun warke kuma an sallamesu a jihoshi talatin da shida na kasarnan, da babban birnin tarayya, Abuja.
- Ƴansanda sun kama mutum mai shekara 60 kan zargin yi wa yarinya fyade a Bauchi
- An daure ‘yar Najeriya shekaru 70 a Amurka kan badakalar tallafin yara
- Mayaƙan Lakurawa sun kashe jami’an kwastam biyu a Kebbi
- Tinubu Ya Amince Najeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taron Shugabannin Hukumomin Ƙwallon Ƙafa Na Afirka
- Kwastam Da NDLEA Sun Kama Tabar Wiwi Ta Naira Biliyan 16.6 Da Aka Yi Fasa Kwaurinta Zuwa Najeriya
Cutar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu cikin sa’o’i ashirin da hudu, kuma yawan wadanda annobar ta kashe kawo yanzu ya kai dari tara da tamanin da daya.
Hakan ya fito ne daga hukumar dakile yaduwar cututttuka ta kasa NCDC, wacce ke jagorantar kula da barkewar cutar corona, cuta mai kama da mura, wacce ta yadu zuwa kasashe sama da dari biyu kuma ta harbi sama da mutane miliyan biyu.