Yawan mutanen da annobar corona ta shafa a Najeriya ya kai dubu arba’in da tara da dari takwas da casa’in da biyar, bayan an sake gano mutane dari hudu da goma dauke da cutar a jiya.
Daga cikin adadin, sama da mutane dubu talatin da bakwai sun warke kuma an sallamesu a jihoshi talatin da shida na kasarnan, da babban birnin tarayya, Abuja.
- Akalla mutane 2,000 ne suka amfana tallafin Shinkafa daga AA Rano a karamar Hakumar Hadejia
- Kwamishinan ‘yan sandan Kano ya ziyarci kasuwar Kwalema, inda aka samu tashin gobara
- Gwamnatin jihar Jigawa ta tallafawa mata da rabon awaki 264 a karamar hakumar Birniwa.
- Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sunyi alwashin kalubalantar matakin Tinubu kan jihar Rivers
- Za mu bi hanyoyin da doka ta tanada wurin dawo mana da haƙƙinmu – Fubara
Cutar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu cikin sa’o’i ashirin da hudu, kuma yawan wadanda annobar ta kashe kawo yanzu ya kai dari tara da tamanin da daya.
Hakan ya fito ne daga hukumar dakile yaduwar cututttuka ta kasa NCDC, wacce ke jagorantar kula da barkewar cutar corona, cuta mai kama da mura, wacce ta yadu zuwa kasashe sama da dari biyu kuma ta harbi sama da mutane miliyan biyu.