

Yawan mutanen da annobar corona ta shafa a Najeriya ya kai dubu arba’in da tara da dari takwas da casa’in da biyar, bayan an sake gano mutane dari hudu da goma dauke da cutar a jiya.
Daga cikin adadin, sama da mutane dubu talatin da bakwai sun warke kuma an sallamesu a jihoshi talatin da shida na kasarnan, da babban birnin tarayya, Abuja.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Cutar ta yi sanadiyyar mutuwar mutane hudu cikin sa’o’i ashirin da hudu, kuma yawan wadanda annobar ta kashe kawo yanzu ya kai dari tara da tamanin da daya.
Hakan ya fito ne daga hukumar dakile yaduwar cututttuka ta kasa NCDC, wacce ke jagorantar kula da barkewar cutar corona, cuta mai kama da mura, wacce ta yadu zuwa kasashe sama da dari biyu kuma ta harbi sama da mutane miliyan biyu.