INEC ta bayyana zaben gwamnan jihar Anambra a matsayin wanda bai kammalu ba
Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa wato INEC ta bayyana zaben gwamnan jihar Anambra a matsayin wanda bai kammalu ba.
Farfesa Florence Obi, baturiyar zaben jihar, ta sanar da hakan ne a ofishin hukumar INEC da ke Awka, babban birnin jihar Anambra a sa’o’in farko na ranar Litinin.
Ta ce ba za a iya bayyana wanda yayi nasarar zaben ba saboda ba a yi zabe ba a karamar hukumar Ihiala ta jihar.
A yayin kare abinda suka aikata a dokar zabe, Obi ta ce za a yi zaben maye gurbi a karamar hukumar Ihiala a ranar Talata.