JAMB Ta Sanar Da Ranar 25 Ga Afrilu A Ranar Da Za’a Fara Jarabawar UTME

0 183

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire, JAMB, ta sanar da sabuwar ranar da za a fara jarrabawar gama-gari, UTME, ta 2023.
Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa dauke da sa hannun kakakinta, Fabian Benjamin a Abuja a yau Lahadi.
Benjamin ya ce UTME din, wacce da fari aka shirya za a fara a ranar 29 ga Afrilu, yanzu an janyo ta baya zuwa ranar 25 ga Afrilu, 2023.
Ya kuma ce hukumar za ta ci gaba da gudanar da jarabawar UTME ta gwaji a ranar 18 ga Afrilu, 2023.
Za a iya tunawa tun da farko JAMB ta gudanar da UTME ta gwaji ta 2023 a ranar Alhamis, 30 ga watan Maris a cibiyoyi 725 a fadin kasar nan.
Duk da haka, atisayen ya ci karo da wasu matsaloli na na’urori a wasu cibiyoyi, wanda hakan ya hana wasu ɗalibai damar zana jarrabawar.
An tsara jarrabawar ta gwaji ne da nufin gwada shirye-shiryen hukumar da na abokan aikinta na UTME tare da baiwa ɗalibai damar samun gogewa ta hanyar sanin yanayin yadda ake zana jarabawar ta na’ura mai ƙwaƙwalwa, wato CBT.

Leave a Reply

%d bloggers like this: