

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Kimanin mutane 7 ne aka bada rahotan cewa yan bindigar sun kashe a garin Faru na karamar hukumar Maradun ta Jihar Zamfara.
Wannan na zuwa ne kwanaki 2, bayan yan bindigar sun kashe mutane 48 a karamar hukumar Bakura ta Jihar.
Da ya ke zantawa da gidan Talabijin na Channels Tv, wani shaidar gani da ido ya ce sun kewaye garin Faru a jiya Lahadi da Rana.
A cewarsa, yan bindigar sun kewaye garin ne da misalin karfe 2 na Dare, inda suka din ga harbi kan mai uwa da wabi.
Shima wani shaidar gani da Ido ya tabbatar da mutuwar mutane 7 a garin, inda ya kara da cewa mutane da dama sun samu raunika a lokacin.
Kawo yanzu rundunar yan sandan Jihar ba ta ce komai ba kan kaiwa hare-haren.