- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Ma’aikatar ilmi, kimiyya da fasaha ta jihar Jigawa ta fara rangadin duba makarantu a wani mataki na tabbatar da kyakkyawan yanayin koyo da koyarwa a makarantu.
A sanarwar da maaikatar ta fitar ta hannun mai magana da yawun ma’aikatar, Wasilu Umar Ringim, tace a lokacin ziyarar an tura kwamishina da babbar sakatariya da sauran shugabannin sassan hukumomin ma’aikatar zuwa makarantu domin duba harkokin koyo da koyarwa a makarantun.
Sanarwar tace a lokacin ziyarar, masu duba makarantu zasu lura da harkokin koyo da koyarwa da duba tsarin jaddawalin koyarwa na malaman makarantun.
Sanarwar ta rawaito kwamishinan ilmi, kimiyya da fasaha na jiha, Dr Lawan Yunusa Danzomo, yana kira ga malaman da suke cikin masu ziyarar da su sanya kaimi tare da yin gaskiya da adalci kan abubuwan da zasu gani.