Majalisar dattijai ta fara aikin yi wa dokar Hukumar Kula da Zuba Jari ta Kasa kwaskwarima

0 237

Kudurin dokar wanda Sanata Opeyemi Bamidele ne ya gabatar da ita, na neman mayar da hukumar daga ma’aikatar jin kai da yaki da talauci zuwa fadar shugaban kasa.

Shugaban majalisar dattawan ya ce a yanzu dokar za ta kasance karkashin kulawar shugaban kasa kai tsaye.

Bamidele ya ce gyaran da aka yi wa dokar shirin zuba jari ta kasa, 2023 shi ne don tabbatar da cewa shirin zuba jarin zamantakewa ya kasance daidai, gaskiya, inganci da kuma rikon amana.

Ya bayyana cewa, gyaran ya samo asali ne sakamakon jajircewar sabon bege na shugaban kasa Bola Tinubu na tabbatar da cewa shirin zuba jarin zamantakewa shine tsari, gaskiya, inganci da tsarin bayar da bayanai, isassun daidaito da aiki tare a tsakanin manyan hukumomin gwamnati. Bayan kammala zaman, shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya mika kudurin dokar ga kwamitin koli domin tantancewa domin baiwa ‘yan majalisar damar yin amfani da kudirin dokar ta sashi.

Leave a Reply

%d bloggers like this: