

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Majalisar Zartarwa ta Tarayya a jiya ta amince da Naira miliyan dubu 1 da miliyan 400 domin siyan karin kayan aiki ga Kamfanin Watsa Wutar Lantarki na kasa, a wani bangare na kokarin inganta wutar lantarki a kasarnan.
Amincewar ta zo ne kasa da mako guda bayan da kasarnan ta fuskanci rugujewar tsarin wutar lantarki karo na biyar a cikin watanni uku.
Ministan wutar lantarki, Abubakar Aliyu ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labaran fadar shugaban kasa a karshen taron da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya jagoranta.
Ya ce an amince da kudin kwangilar da tashar wuta da ke Kafanchan a jihar Kaduna, tare da fadada layin wuta a tashar Jos ta jihar Filato. Ya ce ayyukan za su ci kudi kimanin naira miliyan 132 da dubu 700.
Amincewa ta biyu da ya samu ita ce samar da kayan aiki da motocin aiki ga Kamfanin Watsa Wutar Lantarki na kasa akan kudi naira miliyan dubu 1 da miliyan 300.