

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Majalissar dokokin jihar Yobe ta musanta zargin da ake mata, na yunkurin tsige gwamnan jihar Mai Mala-Buni.
Mataimakin shugaban kwamitin watsa labarai na majalissar Alhaji Abdullahi Bazuwa ne ya bayyana hakan a lokacin dayake karin haske a Damaturu babban birnin jihar, tare da karyata labaran yunkurin majalissar na tsige gwamna Mai Mala Buni daga kan mukamin sa.
Kafin hakan dai wasu kafafen yada labarai na yanar gizo sun wallafa cewa, majalissar dokokin jihar na yunkurin tsige mai Mala Buni daga mulkinsa.
Alhaji Abdullahi Bazuwa ya kuma bayyana cewa, yanzu haka majalissar ta maida hanakalinta ne wajan yin ayyukan tare da tabbbatar da kama jaridun da suka buga wannna labarin na kanzon kurege.
Tare da tsabbatar da cewa majalissaar zataci gaba da gudanar da ayyukan ta na yau da kullum kamar yanda aka saba.