Majalisun kasa suna aiki tukuru domin tabbatar da cewa yan Najeriya mazauna kasashen waje suna da damar kada kuri’u a zabe mai zuwa

0 84

Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmed Lawan, ya ce Majalisun kasa, suna aiki tukuru domin tabbatar da cewa yan Najeriya mazauna kasashen waje suna da damar kada Kuri’un su a lokacin zabe.

Sanata Ahmed Lawan, ya bayyana hakan a lokacin da ya karbi bakuncin Shugabar Hukumar Kula da yan Najeriya mazauna kasashen waje Misis Abike Dabiri-Erewa, a ofishinsa dake Abuja.

Shugaban Majalisar ya ce majalisun kasa suna aiki tukuru domin tabbatar da cewa an samu gamsuwa a lokacin zaben.

Haka kuma ya ce suna aiki tukuru domin tabbatar da cewa yan Najeriyar da suke zaune a kasashen waje sun kada kuri’un su, kuma an Kirga su.

A cewarsa, Majalisun suna kokarin kawo sauye-sauyen a fannin zabe, ta yadda hakan zai bawa yan Kasar nan, na ciki da waje damar Kada Kuri’un su.

A jawabinsa, Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, kuma Shugaban Kwamatin Kawo Sauye-Sauye ga Kundin Tsarin Mulkin Kasa na shekarar 1999, Sanata Ovie Omo-Agege, ya ce an umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC ta kawo sauye-sauyen ta yadda hakan zai bawa yan Najeriya mazauna kasashen waje damar zabe.

Leave a Reply

%d bloggers like this: