

Hukumar samarda aiyukan yi ta kasa NDE ta kaddamar da bada horan watanni uku ga matasa maza da maza guda dari a jihar Jigawa.
Shugaban hukumar a jihar nan Malam Abubakar Jamo ya sanar da hakan a lokacin ganawa da manema labarai a garin Dutse.
Yace wasu daga cikin matasan zasu sami horo akan bangarori daban daban na aikin gona.
- Tarihin Gamuwa 10 Tsakanin Kano Pillars VS Eyimba Da Kuma Wasan Yau
- Abubuwa 5 da suka zama wajibi lokacin sanyi
- An ƙaddamar da kudin kariya ga ƴan jarida da masu fafutukar ƴancin amfani da yanar gizo
- Yadda ake duba suna don zama ma’aikacin damara na 2020 a Nijeria
- Me Ƙungiyar Izala ta ce kan matsalolin tsaro a Najeriya?
Mallam Jamo ya kara da cewar ana gudanar da bada horan ne karkashin shirin bada horo a yankunan karkara.
Inda yace matasan za a tura su wuraren koyan sanin makamar aiki na makonni biyu a gonaki.
Mallam Abubakar Jamo ya shawarci matasa dasu shiga cikin shirin domin samun hanyoyin dogaro da kai.