Kungiyar Kwadago ta Kasa NLC da takwararta ta TUC a jiya sun yi watsi da hukuncin da kotun ma’aikata ta yanke wanda ya hana su tafiya yajin aiki farawa daga ranar Litinin.
Kungiyoyin na NLC da TUC sun sanar da haka bayan wata ganawa tsakanin gwamnatin tarayya da ma’aikata wanda aka tashi ba a cimma matsaya ba a jiya da yamma.
Biyo bayan karin farashin kudin wuta da na man fetur, gwamnati da kungiyoyin kwadago sun gana a ranar Talatar satin da ya gabata, a zaman an tashi baram-baram saboda kin amincewar gwamnati na janye karin kudaden, ko kuma bai wa ma’aikata tallafin rage radadin illar hakan.
- Barcelona ta ba Lamine Yamal lamba 10
- An ɗaura auren Umaru Musa Yar’Adua Jnr., ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Umaru Musa Yar’Adua, tare da amaryarsa Maryam Ayuba Shuaibu
- Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar (GCON), ya kawo karshen shakku da tsokaci, inda a hukumance ya fice dga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP),
- Manhajar TikTok ta goge fiye da bidiyo miliyan 3.6 a Najeriya saboda saba ka’idar dokokinta
- Tsohon Shugaban APC na ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Edo, ya fice daga jam’iyya APC zuwa jam’iyyar hadaka ta ADC
Kungiyoyin na NLC da TUC daga nan suka ayyana tafiya yajin aiki da zanga-zanga wanda za a fara ranar Litinin mai zuwa. Dukkan kungiyoyin sunce zasu hada kai domin tabbatar da yajin aikin sosai.