Gwamantin jihar Jigawa ta amince a bude makaratun fririmare da na sakandire a ranar litinin 26 ga watan nan a fadin jiha.
Kwamishinan yada labarai na jihar nan Malam Ibrahim Mamser ne ya bayyana hakan bayan zaman majalissar zartarwa ta jihar da aka gudanar karkasahin gwamna Muhammadu Badaru Abubakar a gidan gwamanti dake dutse.

A tsarin jadawalin komawar, Yan makarantun kwana zasu koma a ranar lahadi 25 ga watan oktoba, sannna bayan kwana daya sauran yan makarantun jeka ka dawo su koma a ranar litinin 26 ga watan nan da muke ciki.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sannan ya kara da cewa yaran firimare yan aji 1 zuwa 3 za suna zuwa da safe sannan yan aji 4 zuwa aji 6 zasu na zuwa da yamma.
Kazalika ya kara da cewa yan karamar sakandire zasu na zuwa makarantun su da safe, kana daga bisani yan yan babbar sakandire zasu na zuwa da yamma.