Gwamantin jihar Jigawa ta amince a bude makaratun fririmare da na sakandire a ranar litinin 26 ga watan nan a fadin jiha.
Kwamishinan yada labarai na jihar nan Malam Ibrahim Mamser ne ya bayyana hakan bayan zaman majalissar zartarwa ta jihar da aka gudanar karkasahin gwamna Muhammadu Badaru Abubakar a gidan gwamanti dake dutse.
A tsarin jadawalin komawar, Yan makarantun kwana zasu koma a ranar lahadi 25 ga watan oktoba, sannna bayan kwana daya sauran yan makarantun jeka ka dawo su koma a ranar litinin 26 ga watan nan da muke ciki.
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
Sannan ya kara da cewa yaran firimare yan aji 1 zuwa 3 za suna zuwa da safe sannan yan aji 4 zuwa aji 6 zasu na zuwa da yamma.
Kazalika ya kara da cewa yan karamar sakandire zasu na zuwa makarantun su da safe, kana daga bisani yan yan babbar sakandire zasu na zuwa da yamma.