Mun fara cimma abinda muke so tunda mun fara fitar da taki ga kasashen waje – Gwamnatin Tarayya

0 63

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya danganta karuwar karfin Najeriya na zama jigo a samar da takin zamani a Afirca da yadda gwamnati mai ci ta fara amfani da kudirorin da suka kamata.

Shugaban Kasar ya sanar da haka a yau lokacin da yake karbar bakuncin shugabannin kungiyar masu samar da takin zamani a Najeriya, a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Shugaban kasar yace wannan gagarumin cigaban da aka samu cikin kankanin lokaci ya tabbatar da karuwar kwararowar masu zuba jari zuwa bangaren daga kamfanoni masu zaman kansu, lamarin da ya kawo arziki ga miliyoyin ‘yan Najeriya tare da riba mai yawa ga masu zuba jarin.

Ya bayyana jin dadinsa kasancewar yanzu an wuce lokacin karancin takin zamani a kasarnan, inda ya yabawa kungiyar bisa hada kai da gwamnati a aikin samar da takin zamani domin cigaban noma.

Shugaban kasar yayi amfani da lokacin wajen tilawar matakan da gwamnatinsa ta dauka da nufin magance dogaro da kasashen waje domin samun takin zamanin da wadatar abinci a kasarnan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: