

- Wasu ‘yan bindiga sun kashe wakilai uku na ‘yan takarar gwamna na jam’iyyar PDP daga karamar hukumar Mariga ta jihar Neja - May 26, 2022
- Dalilan da yasa wasu ‘yan takarar gwamna 2 na jam’iyyar APC suka yi watsi da zaman ganawar da gwamna Badaru ya kira domin a samar da dan takarar daya tal - May 26, 2022
- Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da aka dakatar, Abba Kyari ya garzaya wata babbar kotun tarayya domin neman belinsa - May 26, 2022
Dubban Mutane ne yau Laraba suka sake gudanar da zanga zangar adawa da shirin amincewa da wata doka da zata bada damar tisa keyar wanda ake zargi da aikata laifi daga Hong Kong zuwa China domin yi masa shari’a.
Masu zanga zangar akasarin su matasa da dalibai sun yiwa ofisoshin gwamnati kawanya, inda suka hana motoci motsawa domin ganin Majalisa tayi watsi da dokar.
Ganin yadda tururuwar masu zanga zangar ta mamaye jami’an tsaron da suke cikin damarar ko ta kwana, shugabannin Majalisa sun bayyana dakatar da mahawara kan dokar zuwa wani lokaci nan gaba.

A shekara ta 2017 aka zabi Carrie Lam a matsayin sabuwar shugaba Hong Kong bayan kwamitin da ke goyon bayan China sun kada kuri’ar.
Zaben dai a lokacin ya fuskanci suka daga ‘yan kasar da suke son a ba kowa yancin kada kuri’a, maimakon wasu tsiraru.