

- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami musamman a lokacin gudanar da zabukan fidda gwani na jam’iyyun siyasa.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Lawan Shiisu Adam da ya rabawa manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.
A cewar sanarwar, kwamishinan ‘yan sandan jihar, Aliyu Sale Tafida, ya bukaci ‘yan siyasa da su shawarci mabiyansu da su guji yin hakan, su kuma bi ka’idojin gudanar da zabe.
Kwamishinan ‘yan sandan ya bayyana cewa rundunar ‘yan sandan ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kame duk wanda ke son yin amfani da zaben wajen tada fitina da karya dokar da ke kunshe a cikin dokokin zabe.
A saboda haka, Aliyu Tafida ya yi kira ga mutanen jihar da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu na halal da kuma yin amfani da ka’idojin da aka tanada domin samun sahihin zaben fidda gwani a jihar.