

- Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC ta rufe kamfanonin ruwa guda 10 a jihar Ondo bisa rashin bin ka’idoji - July 4, 2022
- Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AA, Hamza Al-Mustapha, ya ce jam’iyyarsa ba za ta yi hadin gwiwa da mutanen da basu damu da makomar al’umma ba - July 4, 2022
- Yadda wani mutum ya kona matarsa bayan ya gama dukanta a jihar Ogun - July 4, 2022
Ya zuwa yanzu sama da mutane 340 ne aka tabbatar da mutuwarsu a lardin KwaZulu-Natal na kasar Afirka ta Kudu sanadiyyar ambaliyar ruwa a lardin mafi muni cikin shekaru da dama.
Firemiyan lardin, Sihle Zikalala, ya ce kimanin mutane dubu 41 ne lamarin ya shafa a kewayen birnin Durban.
Ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka kwashe kwanaki ana tafkawa ya lalata gidaje da tituna da gadoji, lamarin da ya sa gwamnati ta ayyana dokar annoba a ranar Laraba.
An dawo da wutar lantarki da ruwan sha a wasu yankuna, amma hukumomi na yin kira da a yi hakuri saboda aiki ya yiwa kungiyoyin agaji yawa.
Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa ya dora alhakin matsalar kan sauyin yanayi.