

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Ado Bayero, ya bukaci yan Kasuwar Jihar da kada su kara farashin kayan Masarufi saboda zuwa watan Ramadana.
Sarkin ya yi wannan kiran ne a lokacin da ake gudanar Addu’oi na musamman kan cikarsa shekaru 2 akan Karagar Mulkin Masarautar.
Alhaji Aminu Ado Bayero, ya godewa Allah Subhanahu wata Ala, bisa damar da ya bashi na Jagorantar Al’umma, inda ya bukaci yan kasuwar su ji tsoron Allah karsu kara farashin.
Haka kuma ya godewa Gwamnatin Jihar Kano da Mambobin Majalisar Masarautar da kuma Al’ummar Kano bisa hadin kan da yake samu.
An gudanar da Addu’oi a babban Masallacin Kano, wanda babban Limamin Kano Farfesa Muhammad Sani Zahraddeen da Wazirin Kano Alhaji Sa’ad Shehu Gidado, suka jagoranta.