

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Dan majalisar Dattawa mai wakiltar Jigawa ta tsakiya, Senator Sabo Muhammad Nakudu, ya bada gudummawar kwamfutoci ga dalibai 35 ga dalibai biyar-biyar na kananan hukumomin 7 da yake wakilta wadanda suke karatu a manyan makarantu daban-daban.
Da yake mika kwamfutocin ga daliban a ofishin Kungiyar ci gaban masarautar Dutse, Senator Sabo Nakudu ya ce ya bada kwamfutocin ne da nufin taimakawa daliban wajen harkokin karatunsu bisa la’akari da yadda fasahar tattara bayanai da sadarwa ke da tasirin a wannan zamani.
Sanatan wanda ya samu wakilcin mai taimakawa gwamna kan harkokin kananan hukumomi Alhaji Khalid Ibrahim, ya bukaci daliban su yi amfani da kwamfutocin kamar yadda yakamata domin samun nasarar a harkokin karatunsu.
A jawabinsa na maraba, shugaban kungiyar cigaban masarautar Dutse, Khadi Isa Jibrin Gantsa, ya ce kungiyar tana kokarin fadakarwa da kuma jawo hankalin al’ummomin masauratar domin suyi aiki tare wajen kawo cigaba mai dorewa ba tare da la’akari da siyasa ko yanki ba inda ya bukaci mawadata su bada gudummawa sosai wajen bunkasa harkokin ilimi.
A nasa jawabin, Sakataren kungiyar Dakta Ado Garba Jangargari, ya yabawa Senator Sabo Muhammad Nakudu bisa mu’amala da kungiyar wajen samar da ababen more rayuwa ga jama’a inda ya bukaci fitattu daga cikin al’ummomin masarautar Dutse da ke cikin gwamnati ko kasuwanci da su hada kai da kungiyar wajen aiwatar manofifin cigaba.
Da suke jawabi a madadin daliban da suka amfana, Abdul’Aziz Umar Jahun na jami’ar tarayya dake Dutse da kuma
Ummukhulthum Umar Abbas da ke jami’ar Sule Lamido Kafin Hausa, sun godewa Sanatan bisa wannan gudummawa inda suka roki fitattu a cikin al’umma da ‘yan kasuwa da su tallafawa harkokin ilimi.