

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a yau ya rantsar da kwamishinoni 6 na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC).
Kamfanin dillancin labarai na kasa ya bayar da rahoton cewa bikin rantsuwar yazo ne kafin fara zaman majalisar zartarwa ta tarayya da aka gudanar a zauren majalisar dake fadar shugaban kasa a Abuja.
Kwamishinonin hukumar na kasa sune Mohammed Haruna daga Neja, May Agbamuche-Mbu daga jihar Delta, Ukaegbu Nnamdi daga jihar Abia, Abubakar Alkali daga jihar Adamawa, Rhoda Gumus daga jihar Bayelsa da kuma Sam Olumekun daga jihar Ondo.
Wadanda suka halarci bikin rantsuwar kwamishinonin sune mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, shugaban majalisar dattawa, Ahmed Lawan, da kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila.
Sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha, da shugaban ma’aikatan shugaban kasa, Ibrahim Gambari, da wasu ministoci tare da shugaban hukumar ta INEC, Mahmoud Yakubu, sun shaida rantsar da kwamishinonin na INEC.