Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da harin bom da aka kai wa jirgin ƙasa na hanyar Kaduna zuwa Abuja

0 174

Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da harin bam da aka kai wa jirgin kasa da ke ɗauke da fasinja kusan 1000 a hanyar Abuja zuwa Kaduna, yana mai bayyana al’amarin a “matsayin wani abin damuwa matuka.”

A cikin sanarwar da fadar shugaban ta fitar, Buhari ya ce, “kamar sauran ‘yan Najeriya, ina cikin jimami matuƙa da faruwar wannan lamarin, wanda shi ne irinsa na biyu, wanda ya kai ga sanadin mutuwar fasinjojin da har yanzu ba a tantance adadinsu ba da kuma wasu da suka samu raunuka.”

“Harin da aka kai kan jirgin kasa, abin takaici ne; tunani na yana kan iyalan waɗanda suka rasu da kuma addu’a ga wadanda suka jikkata,” in ji Buhari.

Shugaban ya ce ya bayar da umarnin gaggawa na tabbatar da bincike da hanyoyin magance matsalar tsaron titin jigin ƙasa na Abuja zuwa Kaduna.

Sannan ya umarci jami’an tsaro su kuɓutar da fasinjojin da daka sace tare da farautar ƴan bindigar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: