- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari yayi ganawar sirri da daukacin ‘yan takarar shugabancin jam’iyyar APC a babban taronta na kasa da za a gudanar a ranar Asabar mai zuwa.
Mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan daukar hoto, Sunday Aghaeze, ya tabbatar da hakan da yammacin jiya.
Kamfanin Dillancin Labarai na Kasa ya bayar da rahoton cewa, ‘yan takarar sun samu jagorancin shugaban riko na kwamitin rikon kwaryar jam’iyyar APC kuma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni.
Kamfanin Dillancin Labaran ya bayar da rahoton cewa, wadanda abin ya shafa sun hada da George Akume, Tanko Al-makura, Sani Musa, Abdullahi Adamu, Mohammed Saidu-Estu, Abdulaziz Yari da Ali Modu Sheriff.
An rawaito cewa sakataren gwamnatin tarayya, Boss Mustapha da shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Ibrahim Gambari suma sun halarci zaman ganawar shugaban kasar tare da ‘yan takarar.