

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Shahararren limamin coci, Tunde Bakare, ya yi wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Bayan ganawar, Tunde Bakare ya shaidawa manema labarai cewa ya tattauna batutuwa daban-daban tare da shugaban kasar, ciki har da bukatar sake fasalin kasarnan da kuma burin siyasarsa a nan gaba.
Tunde Bakare abokin Shugaba Buhari ne kuma abokin takararsa a zaben shugaban kasa na shekarar 2011 wanda ya sha kaye a hannun shugaba mai ci a lokacin, Goodluck Ebele Jonathan.
Babban malamin addinin kiristan, ya yi ta sukar gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ‘yan kwanakinnan.
Lokacin da aka tambaye shi ko zai tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2023, Tunde Bakare ya ki bayar da cikakkiyar amsa, sai dai ya ce ya sanar da niyyarsa ga Shugaban Kasa Muhammadu Buhari.