

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Wasu ‘yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe ‘yan sanda uku da wani dan achaba a garin Suleja na jihar Neja.
An rawaito cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na daren jiya.
Rahotanni sun ce ‘yan sandan na amsa kiran gaggawa ne a lokacin da aka yi musu kwanton bauna a kusa da wani wuri da ake kira Old Barracks.
Shugaban Karamar Hukumar Suleja, Alhaji Abdullahi Shuaibu Maje, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce kimanin mutane uku ne suka tsira daga harin, ciki har da dan kato da gora.
Ya ce yanzu haka suna jinya a wani asibiti da ke yankin.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Wasiu Abiodun, bai amsa kiran waya da sakon da aka aika masa dagane da batun ba.