Wasu yan bindiga sun kai farmaki karamar hukumar Malumfashi a jihar katsina inda sun kashe akalla mutane 17

0 83

Wasu yan bindiga sun kai farmaki a mazabar karfi dake karamar hukumar Malumfashi a jihar katsina, an rawaito sun kashe akalla mutane 17.

Wata majiya a yankin ta shaidawa manema labarai cewa yan bindigar kai hari cikin kauyuka akalla 5 duka karkashin mazabar ta Karfi a jiya juma’a, inda suka yi ta Harbin kan mai uwa da wabi kan mutanen kauyukan, lamarin da yayi sanadiyyar mutuwar mutane 17 tare da jikkata da dama.

A cewar majiyar yan bindigar sun isa yankunan da misalin karfe 11 na daren jiya juma’a, suka fara harbe-harben tare da sace mutane.

Wani dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar a majalisar dokoki ta jihar Aminu Ibrahim Saidu, wanda ya tabbatar da al’amarin yace ziyarci yankunan da lamarin ya faru domin yin alhini ga iyalan da suka hadu da ibtila’in.

Leave a Reply

%d bloggers like this: