- Gwamna Zulum ya raba wa likitoci fiye da 80 didaje da kudi Naira miliyan 79 don inganta rayuwarsu - July 2, 2022
- Manyan Sarakunan kasar Yarabawa sunyi kiran samun zaman lafiya daga gwamnati kafin zaben 2023 - July 2, 2022
- Kasar Jamus za ta fara dawo wa da Najeriya dubban kayayyakin tarihin ta da aka wawushe tun lokacin mulkin mallaka - July 2, 2022
Wasu ‘yan bindiga sun kashe ‘yan kungiyar ‘yan banga hudu a Awka, babban birnin jihar Anambra.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 4 da rabi na yamma.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Anambra, Tochukwu Ikenga, a wata sanarwa da ya fitar a yau, ya ce ‘yan sanda sun mayar da martani kan harin da aka kai wa ‘yan banga.
Kakakin ‘yan sandan ya ce an yi artabu tsakanin ‘yan bindigar da jami’an ‘yan sandan da suka amsa kiran gaggawa.
Kakakin ‘yan sandan ya ce, a wani lamari na daban, ‘yan sandan sun ceto wani da aka yi garkuwa da shi.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu ‘yan bindiga biyar ne suka sace mutumin a makon da ya gabata inda daga bisani suka bukaci a biya naira miliyan 10 na kudin fansa.