

- Mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Mallam Umar Namadi, shine ya lashe zaben fidda gwani na dan takarar gwamna a jam’iyyar APC - May 27, 2022
- Shugaba Buhari yace gwamnatinsa tana assasa ginshiki mai inganci na kyakykyawar rayuwa domin yara manyan gobe a Najeriya - May 27, 2022
- Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta haramta bangar siyasa da tare da yin amfani da duk wani makami ga yaran yan siyasa - May 27, 2022
Yan ta’adda sun kai hari a kauyukan Gwada da ke karamar hukumar Shiroro a jihar Neja a lokacin da musulmi suke shirin buda baki, na azumin watan Ramadana a ranar Asabar.
Kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN ya tattaro cewa maharan sun kashe mutane hudu tare da yin awon gaba da mutanen da ba a tantance adadinsu ba.
Kakakin Gamayyar Kungiyoyin Shiroro, Salisu Sabo, wanda ya tabbatar wa da wakilinmu harin ta wayar tarho, ya ce ‘yan ta’addan sun shafe sa’o’i da yawa suna ta’addanci a cikin al’umma.
Ya ce ‘yan ta’addan sun fatattaki al’ummomin da ke kan hanyar Gwada zuwa Shiroro.
Al’ummomin sun hada da Tapila, Kwakwa, Kadna da kuma garin Gwada, wanda yana daga cikin wuraren da babu tsaro a karamar hukumar Shiroro.
Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta kawo musu dauki ta hanyar tura karin jami’an tsaro a yankin.