‘Yan bindiga a daren jiya sun kashe akalla mutane 20, tare da yin garkuwa da wasu da dama a Gatawa, wani kauye a karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto.
Ana kallon kauyen na manoma a matsayin daya daga cikin kauyukan da ke da tsaro a gabashin jihar, inda ‘yan ta’adda suka yi ta kai hare-hare.
Mummunan harin ya zo ne sa’o’i 24 bayan wani a Gangara, cikin wannan karamar hukumar.
Wani mazaunin yankin mai suna Bashir Gobir, ya ce kanwarsa na cikin wadanda aka sace.
Bashir Gobir ya ce bai san adadin mutanen da aka kashe a harin ba.
Da aka tuntubi mai magana da yawun ‘yan sanda a Sakkwato, Sanusi Abubakar, ya ce yana halartar wani taro kuma ya yi alkawarin zai biyo kiran.