Cutar kwalara tayi ajalin mutum 169 a Kano, 191 a kwance a asibiti

0 76

Gwamnatin Jihar Kano ta ce ɓarkewar cutar kwalara a kananan hukumomin ta guda 44 na jihar ya yi ajalin mutane 169, yayinda 191 ke kwance a asibiti a halin yanzu.

Kamar yadda BBCHausa ta ruwaito, Darakta a fanin lafiyar al’umma a ma’aikatar lafiyar jihar, Dr Ashiru Rajab ya shaida cewa an tattaro waɗanan alkaluma ne a cikin watannin uku, sannan ya ƙara da cewa mutum 5,221 suka kamu da cutar, cikinsu 4,860 sun samu sauki kawo yanzu.

Saidai a cewarsa, mutum 191 da ke kwance yanzu a asibiti na samun kulawa a asibitocin gwamnati dake wadannan kananan hukumomin.

Dr Rajab ya yi kira ga al’umma da su kula da tsafta da abubuwan da suke ci, musamman mazauna karkara domin kare kai.

Leave a Reply

%d bloggers like this: