Gwamnatin Jigawa Ta Musanta Alkaluman Da Suka Sa Ka Nuna Tana Cikin Jihohi Masu Fama Da Talauci

0 92

A wani labarin kuma, gwamnatin jihar Jigawa ta musanta rahotannin da suka fito daga hukumar kula da alkaluman lafiya ta kasa da ta sanya jihar a cikin jihohin da suka fi fama da talauci a kasarnan.

Mataimakin gwamnan jihar kuma zababben gwamnan jihar mai jiran gado, Malam Umar Namadi, ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai jim kadan bayan ya karbi rahoton kananan kwamitocin mika mulki.

Umar Namadi ya bayyana cewa gwamnati mai ci a karkashin Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ta bullo da tsare-tsare da shirye-shirye da dama domin rage radadin talauci da ake fama da shi a jihar. Ya jaddada kudirin sa na ci gaba da aiwatar da dukkan kyawawan manufofi da tsare-tsare na gwamnatin Gwamna Muhammad Badaru Abubakar domin ci gaban jihar.

Leave a Reply

%d bloggers like this: