

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Jami’ar Sule Lamido dake Kafin Hausa ta bayar da tallafin sanadaran wanke hannu dake kashe kwayoyin Cututtuka ga gwamnatin jihar Jigawa a wani yunkurin bayar da nata tallafin don dakile yaduwar cutar Korona.
Da yake mika kayan tallafin ga shugaban kwamitin karta kwana kan yaki da Korona a ranar Laraba 15 ga watan Afrilu shugaban jami’ar Farfesa Lawan Sani Taura yace an gudanar da zurzurfan bincike a tsangayar kimiyya ta jami’ar kafin samar da sinadarin mai karfin kashe cututtuka da kaso 99.9.

Ana shi bangaren da yake karbar gudummawar sinadaran wanke hannun har guda 500, Shugaban kwamitin Kwamishinan ma’aikatar lafiya ta jihar Jigawa Dr. Abba Umar Zakari ya yaba da kokarin jami’ar na kirkirar wannan sinadari, inda ya roki jami’ar da ta kara matsa kaimi wurin binciken wasu sinadaran na yaki da cutar don gamawa da ita baki daya.
