Jam’iyyar NNPP Ta Bukaci A Sake Zaben Gwamnan Jihar Borno

0 95

Jam’iyyar ta shigar da kara a gaban kotun sauraron kararrakin zaben gwamna ta nemi a sake zaben gwamnan jihar Borno.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta bayyana gwamnan jihar mai ci, Babagana Umara Zulum a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

Sai dai a yayin da take kalubalantar sakamakon zaben, jam’iyyar NNPP a cikin wata kara da ta shigar ta yi ikirarin cewa hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta cire sunan dan takararta Umar Alkali da tambarin jam’iyyar a cikin takardun zabe.

Sakataren kotun, Mista Taiwo Adediji, ya ce kotun ta karbi kararraki 10 na zaben ‘yan majalisar dokokin kasar.

Ya ce wadannan sun hada da koke-koke guda uku na neman kujerar Sanata da bakwai na majalisar wakilai.

Ya tabbatar da koke guda biyu daga ‘yan takarar jam’iyyar PDP a mazabar Askira/Uba da Kala-Balge na kalubalantar nasarar da ‘yan takarar APC suka samu a yankin.

Leave a Reply

%d bloggers like this: