

- Yadda yan IPOB suka kashe ‘yan Arewa 10 ciki har da mace mai juna biyu da ‘ya’yanta 4 da wasu mutane 6 a jihar Anambra - May 24, 2022
- Sama da mutane 30 ne aka ruwaito sun bace a jihar Borno bayan da wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai musu hari - May 24, 2022
- Tsohon gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, ya karbi tikitin takarar Sanatan Gombe ta Arewa domin tsayawa takara a jam’iyyar PDP a 2023 - May 24, 2022
Kungiyar manoman shinkafa ta kasa (RIFAN) na shirin gudanar da bikin shinkafa a Abuja da nufin tallafawa yunkurin gwamnatin tarayya na wadatar da abinci a kasarnan.
Ana sa ran za a gudanar da bikin a harabar cibiyar kasuwanci da masana’antu ta Abuja, kuma tuni aka yi nisa a shirye-shiryen samun nasarar bikin.
A wani batun kuma, hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta kasa (NCDC) ta sanar da mutuwar karin mutane 6 sanadiyyar cutar corona tare da samun sabbin mutane 670 da suka harbu da cutar a jihoshi 10 na kasarnan da babban birnin tarayya.
Hakan na kunshe ne cikin bayanin da hukumar ta wallafa a shafinta na Facebook yau da safe.
Da sabbin wadanda suka harbu, yawan wadanda cutar ta yi ajalinsu a kasarnan sun kai dubu 3 da 45, yayin da jumillar wadanda cutar ta harba suka karu zuwa dubu 244 da 120.
Kamar yadda alkaluman na NCDC suka nuna, an sallami mutane dubu 216 da 180 bayan sun warke a fadin kasarnan, yayin da har yanzu mutane dubu 24 da 859 suke samun kulawar likitoci.