Kwastam Zata Fara Rufe Shagunan Dake Sayar Da Shinkafar Waje A Kano Da Jigawa

0 117

Hukumar dake yaki da Fasakwauri ta Kasawato Kwastam ta shirya tsaf domin kulle  duk wani shagon da aka kama ya sayar da shinkafar kasar waje da sauran abubuwan da gwannatin kasar nan ta hana shigo daso a fadin Jihohin Kano da Jigawa.

Bayanan hakan na kunshe cikin wata takarda mai lamba NCS/KAN/053/S.28 da hukumar ta rubuta zuwa ga Manyan shagunan dake fadin Jihohin Kano da Jigawa a ranar 17 ga watan Janairun shekarar 2020 da muke ciki,

Inda take Umurtar su da su dakatar da duk wata hulda da kayayyakin kasar wajen da hukumar ta hana shigo dasu ko kuma su fuskanci fushin hukumar na rufe shagunan.

Manufar wannan hukuncin dai sh ine kawo karshen fasakwaurin  kayayyakin kasashen waje zuwa kasarnan da nufin habbaka tattalin arzikin Nijwriya tare da inganta tsaron kasar.

Tun bayan garkame iyakokin kasar nan da gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari tasa akai watanni kadan da suka gabata ne dai, hukumar kwastom da sauran Jami’an tsaro a iyakokin jihar jigawa suke fama da masu fasa kwaurin kayyayakin kasashen waje zuwa kasar nan.

Leave a Reply

%d bloggers like this: