Kimanin ‘yan Najeriya 200,000 suke rasa rayukan su a duk shekara wanda yawancin su yara ne sanadiyyar cututtuka dake da nasaba da abinci a cewar ministan ƙere-ƙere da kimiyya na ƙasar Uche Geoffrey Nnanji.Ministan ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis yayin kaddamar da littafin kiyaye abinci na masu sana’ar siyar da abinci a kasuwanni da kan tituna wanda ya ce hakan na taba tattalin arzikin ƙasar.