Ofishin hukumar hana safarar mutane ta kasa na shiyyar Kano ya kama wasu mutane uku a Kano bisa zargin sayar da wani yaro dan shekara daya a jihar Imo.
Wadanda ake zargin sune kwamandan Hisbah na Fagge, Jamilu Mohammed, da dagacin Fagge, tare da wata mata mai suna Loveth wacce ta sayi yaron.
Shugaban ofishin shiyyar, Shehu Umar, ya gayawa manema labarai cewa an gayyaci wadanda ake zargin domin amsa tambayoyi dangane da lamarin.
- Gwamnati na shirin farfado da masaku da nufin bunkasa noman auduga da samar da tufafi
- Hukumomi na aiki da jami’an tsaro wajen kamo duka ragowar fursunoni 109 da suka tsere daga gidan gyaran hali
- Za’a gudanar da cikakken bincike don tabbatar da ingancin duka jiragen sama da ke zirga-zirga a Najeriya
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
An gano cewa yaron da aka sayar, iyayensa ne suka jefar da shi, kuma ake kula da shi a hukumar Hisbah.
Sai dai, an zargin kwamandan Hisbah ya hada baki da dagacin inda suka sayar da shi. A cewar shugaban hukumar, yaron wanda ake zargin kwamandan Hisbah tare da dagacin Fagge sun sayar da shi ga Loveth, an ceto shi daga hannun mahaifiyar Loveth a jihar Imo.