Shugaba Buhari Yace Masu Kada Kuri’a Sune Sarakuna A Lokacin Zabe

0 62

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce gazawar da gwamnoni 10 suka yi a majalisar dattawa a zaben 2023 na nufin babu tabbacin hanyar da za a bi don samun mulki.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu, ya fitar a jiya a lokacin da ya karbi bakuncin sabon Sarkin Dutse, Alhaji Muhammad Hamim Nuhu Sunusi a fadar gwamnati da ke Abuja.
Ya ce zabukan 2023 sun tabbatar da karuwar dimokuradiyyar musamman yadda masu kada kuri’a a Najeriya suke yi wajen zaben shugabanni.
Bayan ya saurari mai martaba sarkin da ya lissafo wasu ayyuka da gwamnati ta yi wa jihar Jigawa a karkashin gwamnatin shugaban kasa Buhari, da kuma bukatar a kara wasu.
shugaban ya yi alkawarin yin iyakar kokarinsa ga jihar a sauran lokacin da ya rage, kuma zai yi wa shugaban kasa mai jiran gado Asiwaju Bola Ahmed Tinubu bayani, a kan wadancan bukatu, inda ya cewa matsalar samar da ruwan sha a Dutse na da matukar damuwa.
Sarkin ya mika godiyarsa ga gwamnatin Muhammadu Buhari kan yadda jihar Jigawa ta yi fice a fannin noman shinkafa, da amincewa da hanyar layin dogo zuwa Dutse daga Kano da kuma tabbatar da zaman lafiya a jihar, daukacin al’ummar kasa da ma makwaftan da suka fuskanci rashin tsaro a baya. .
Ya kuma tunatar da irin rawar da Najeriya ta taka wajen ‘yantar da kasar Angola, ganin yadda kasar ta yi amfani da girmanta da albarkatunta wajen taimakawa ‘yan uwantaka na Afirka.

Leave a Reply

%d bloggers like this: